Katsina: Dakarun sojoji Sun Kashe Wasu ‘Yan Bindiga

Rundunar Operation Hadarin Daji ta samu nasarar kashe ‘yan ta’adda 5 a karamar hukumar Faskari da ke jihar Katsina.

Kakakin rundunar soji, John Enenche, ya sanar da hakan a Abuja, inda yace rundunar ta samu nasarar ceton mata 3 da yaransu.

Sai dai, daya daga cikin jaruman sojojin ya rasa ransa yayin kokarin ceton wata mata mai shayarwa, a cewar John Enenche Rundunar Operation Hadarin Daji sun ragargaji ‘yan bindiga 5, sun samu nasarar ceton mata 3 da yaransu a kauyen Diskuru da ke karamar hukumar Faskari da ke jihar Katsina, Daily Nigerian ta ruwaito.

Manjo janar John Enenche, kakakin rundunar soji, ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja, yayin da yake bayar da jawabi a kan yadda sojojin arewa maso yamma da sauran wurare a Najeriya suke tafiyar da ayyukansu tsakanin ranar 31 ga watan Oktoba zuwa 4 ga watan Nuwamba

. “Sai dai wani jarumin soja ya rasa rayuwarsa wurin kokarin ceto wata mata mai shayarwa,” cewar Enenche.

Enenche ya ce rundunar ta samu nasarar kama wasu mutane 2 da ake zargin sun hada kai da wasu ‘yan ta’adda da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina, da wasu ‘yan ta’adda 2 da ke karamar hukumar Maru da ke jihar Zamfara.

“Ga dukkan alamu, sojojin Najeriya na iyakar kokarin ganin sun kawo karshen ta’addanci a Najeriya,” a cewarsa.

Enenche ya ce ba kashe ‘yan ta’addan kadai rundunar sojin take yi ba, ta samu nasarar amsar miyagun makamai da dama daga hannunsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here