Jami’an Tsaro Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane a Abuja

 

Rundunar ƴansandan Najeriya a Abuja, babban birnin ƙasar ta ce ta kama wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutanen ne domin neman kuɗin fansa a wani yanki na birnin.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta hannun mai taimaka mata kan hulda da jama’a, Josephine Adeh, rundunar ta ce ta samu nasarar hakan ne a wani samame da ta kai a wani Otal da ke ƙauyen Bassa, bayan samun wasu bayanan sirri.

Abuja, babban birnin Najeriya na fuskantar matsalar tsaro a cikin watanni na baya-bayan nan.

Matsalar garkuwa da mutane da kashe-kashe na ƙara ƙamari, lamarin da ke janyo suka daga ɓangarori da dama.

Cikin sanarwar, rundunar ta bayyana sunan wasu matasa maza guda huɗu da mata biyu, waɗanda ta ce a cikin su akwai waɗanda suka yi ƙaurin suna wurin satar al’umma.

Sanarwar ta ƙara da cewa kayan da aka samu a hannun waɗanda aka kama sun haɗa da bindiga ƙirar AK47 guda ɗaya da wayoyin hannu 10 da kuɗi naira 345,000.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com