‘Yan Sanda Sun Kama Mutumin da ya Cinna wa Dakin ‘Ya’yan Matarsa Wuta

 

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya ta kama wani mutum bisa zargin kunnawa ‘ya’yan matarsa wuta.

Jami’in hulda da jama’a a rundunar ‘yan sandan jihar SP Funmilayo Odunlami ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran kasar faruwar lamarin a Akure babban birnin jihar.

Ya ce lamarin ya faru ne ranar Asabar, inda ya ce jami’an ‘yan sanda suna gudanar da bincike, yayin da yaran ke samun kulawar likitoci a babban asibitin Owo.

Ya kara da cewa an mayar da batun zuwa ga sashen binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar, domin gudanar da bincike yadda ya kamata.

Wani shaida ya fada wa kamfanin dillacin labaran kasar NAN cewa mutumin ya kunna wuta a dakin da yaran ke kwance ne sakamakon samun ‘yar rashin jituwa da matar tasa.

Majiyar ta kara da cewa daya daga cikin yaran ya rasa ransa, sakamakon wutar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here