Zan Karfafa Cin Naman Alade a Madadin Naman Shanu a Jahata – Gwamna Rotimi Akeredolu

 

Gwamnan jahar Ondo ya bayyana aniyarsa ta karfafa maciya naman alade a duk fadin jahar.

Ya ce gwamnatinsa a shirye take don maye gurbin naman shanu da naman alade a fadin jahar.

A cewarsa, jahar na asarar kudaden da ya kamata a jahar za a kashesu ga wasu jahohin daban.

Gwamnan jahar Ondo, Oluwarotimi Akeredolu, ya ce gwamnatinsa za ta karfafa cin naman alade a madadin naman shanu don tattala miliyoyin nairorin da jahar ke asara ga sauran jahohin da ke samar da naman shanu da sauran nau’ikan nama, Daily Trust ta ruwaito.

Akeredolu ya fadi haka ne a ranar Litinin yayin kaddamar da wani babban mayankar alade ta Dutchman Piggery da kayan tallafi a Ilutoro da ke karamar hukumar Akure ta Arewa a jahar a matsayin wani bangare na ayyukan cikarsa kwanaki 100 a ofis.

A cewar gwamnan, kudin da ake kashewa ga wasu jihohin da ke samar da shanu da sauran nau’ikan nama zasu kasance a jihar don kara tattalin arzikin jahar.

Ya kuma ce baya ga ayyukan ta da zai samar wa matasa, za a karfafawa masu cin naman alade, naman alade kuma zai zama madadin naman shanu a jahar.

“Bugu da kari, za a kuma karfafa yankunan mu na karkara don ci gaba.

“Abin mamaki ne cewa miliyoyin Nairori suna barin wannan Jaha duk mako saboda cin naman shanu.

A baya an samu tangarda tsakanin gwamnatin jahar ta Ondo da makiyaya dake zaune a yankunan jahar, lamarin da ya kai ga ba da umarnin fatattakar makiyaya a fadin Ondo, Vanguard ta ruwaito.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here