Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Jagoran ‘Yan Adawa a Cambodia

An haramtawa jagoran ‘yan adawa a Cambodia Kem Sokha duk wani abu da ya shafi siyasa tare daurin shekaru 27 a gidan kaso kan laifin cin amanar kasa.

Ana kallon Kem Sokhaa matsayin babban mai kalubalantar gwamnatin firaiminista Hun Sen.

An zarge shi da hada kai da gwamnatocin kasashen waje, da jam’iyyarsa ta Cambodia National Rescue Party da aka kawo karshenta a 2017.

Sai dai a Kem Sokha ya musanta zarge-zargen da ake ma sa.

Amurka ta yi gaggawar kin amincewa da hukuncin, wanda ya zo watanni kadan gabannin kasar Cambodia ta gudanar da zabe.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here