Wakilan Hukumar leken Asiri ta Pakistan Sun Isa Kabul
Shugaban hukumar leken asiri ta Pakistan laftanar janar Faiz Hameed ya ce wakilan hukumar su isa Kabul, lokacin da ake tsaka da yunkurin kafa gwamnati a Afghanistan.
Read Also:
Kamfanin dillancin labarai na Pakistan ya ce wakilcin wasu manyan jagorori da Janar Faiz Hameed ke jagoranta suna wata tattanawa kan yadda gwamnatin Taliban za ta kasance.
Wani rahoto na cewa shugaban ISI zai tattauana da manyan kwamandoji da kuma shugabannin Taliban.
Kamar yadda jaridu ke rawaito wa Pakistan da Afghanistan za su hadu da shugabannin Taliban domin tattaunawa kan maganar tsaro da tattalin arziki da wasu batutuwa masu mahimmanci.