ƙara Farashi: Hukumar PCACC ta Kama Manajojin Gidan Man Fetur 4 a Jahar Kano

 

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano a Najeriya (PCACC) ta kama manajojin gidajen man fetur huɗu saboda zargin su da sayar da man fiye da farashin da aka ƙayyade na N165 kan lita ɗaya.

Kazalika hukumar ta kama ma’aikatan gidajen mai biyu.

Muƙaddashin Shugaban PCACC Mahmoud Balarabe ya ce sun kama mutanen ne a gidajen mai daban-daban na jihar.

Ya ƙara da cewa sun samu ƙorafe-ƙorafe daga jama’ar gari cewa duk da ƙarancin man da ake fama da shi wasu gidajen mai na sayarwa kan N200 zuwa N208 a Kano.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here