Ƴan Bindiga sun Hallaka Ƴan Sanda Uku a Jihar Edo

 

A ranar Alhamis ne wasu ‘yan bindiga suka kashe jami’an ‘yan sanda uku da jikkata wani guda ɗaya a wani hari da suka kai a jihar Edo.

Bayanai sun ce jami’an bakin aiki ne lokacin da aka yi musu kwanton ɓauna a kusa da garin Agor, kan hanyar Igarra zuwa Auchi na jihar ta Edo.

Rahotanni sun ce an kashe ɗaya daga cikin maharan da jikkata wani daga cikinsu.

An ruwaito cewa an ƙwato bindigogi shida daga hannun maharan.

Lamarin ya faru ne tsakanin karfe 5:30 zuwa 6 na safe kusa da babbar kasuwar Agor.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar ta Edo, SP Chidi Nwabuzor, ya ce har yanzu rundunar ba ta samu cikakken bayani kan harin ba, amma suna ci gaba da bincike.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here