Cutar Corona za ta Daina Barazana ga Lafiyar Al’umma a Bana – WHO

 

Shugaban hukumar lafiya ta duniya WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce yana da kwarin gwiwa a wannan shekarar zai ayyana cutar corona a matsayin annobar da ba ta kai matakin barazanar lafiya ga alummar duniya ba.

Michael Ryan, daraktan sashen ayyukan gaggawa na hukumar WHO ya ce, hukumomin lafiya da dama za su kai matakin da za su bayyana annobar a matsayin barazana ga lafiya wadda za ta ci gaba da kashe rayuka, amma ba za ta iya katse harkokin yau da kullum ba.

Mista Ryan ya ce, za a iya bayyana cutar tamkar wani nau’i ne na mura.

Annobar corona ta hallaka dubban al’umma a sassan duniya tun bayan barkewar ta a farkon shekarar 2020.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here