Mata Sun Fito Zanga-Zanga Kan Adawa da Rufe Makarantun Mata a Afghanistan

Mata da dama sun fito zanga-zanga domin adawa da matakin gwamnatin Taliban na rufe makarantun sakandare na mata.

Matan sun fito rike da kwalaye da ke dauke da bayanin cewa “Ilimi ƴancinmu ne, ba tsarin siyasa ba.”

Sai dai rahotanni sun matan sun watse lokacin da sojojin Taliban suka tunkari wurin da suke zanga-zangar.

Wannan ne karon farko da mata suka fito zanga-zanga a Kabul, makwanni bayan Taliban ta kama mata da dama masu fafutikar kare haƙƙin mata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here